Me yasa Ka'aba ta zama Alqiblar Musulmi? Ga Tarihinta da Hujjojinta
Ka'aba ta zama alqibla ga al'ummar Musulmi bisa wahayin Allah a cikin Suratul Baqarah aya ta 144, a matsayin amsa ga burin Manzon Allah (SAW). Wannan aya tana umarni da a fuskanci Masallacin Harami lokacin sallah, ta maye gurbin alqibla ta farko wato Baitul Maqdis. An sake tabbatar da wannan umarnin a cikin aya ta 149-150.
Canja alqibla ya faru bayan kamar watanni 16-17 daga hijira zuwa Madina, inda kafin nan Manzon Allah (SAW) da sahabbai suke yin sallah suna fuskantar Baitul Maqdis. Manzon Allah (SAW) ya kasance yana fatan a mayar da alqibla zuwa Ka'aba, wanda daga karshe aka karva ta hanyar wahayi.
Hikimar wannan canji dai tana daga ciki jarabawar imani, tabbatar da asalin al'ummar Musulmi, karrama Ka'aba a matsayin gidan ibada na farko, da kuma hujjar cewa shari'a ta fito daga Allah. Ka'aba ita kanta Annabi Ibrahim (AS) da Annabi Isma'il (AS) suka gina ta, tare da harsashin farko daga Annabi Adam (AS).
https://mozaik.inilah.com/dakw