Labari mai raɗaɗi
Abin takaici ne ganin hanyar ceton rayuka da ke da muhimmanci ana tura ta gefe, musamman lokacin da mutane da yawa suka dogara da ita. Ta yaya za mu bar siyasa ta hana bayar da agaji?
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya ya ce Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Falasdinawa ta kusa ‘karya’
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres a ranar Talata ya bukaci kasashe su rufe gibin dala miliyan 100 na kudaden da ake bukata ga hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Falasdinawa ta Majalisar Dinkin Duniya UNRWA, yana mai cewa hukumar na daf da karyewa bayan tsauraran matakan rage kashe kudi da tsuke bakin aljihu. Guterres ya shaida wa wani taron wucin gadi na babban zauren Majalisar kan gudunmawa na son rai cewa halin da UNRWA ke ciki na kara tsananta saboda tsauraran takunkumi a duk fadin yankin Falasdinawa da aka mamaye wanda ke kawo cikas ga aikinta, da kuma babban gibin kudade.