Tambaya game da taƙawa ga Abu Huraira Allah ya yarda da shi
Wani mutum ya zo wurin Abu Huraira Allah ya yarda da shi ya tambaye shi: Me ake nufi da taƙawa? Sai Abu Huraira ya amsa da tambaya: Ko ka taɓa tafiya a hanya mai cike da ƙaya? Mutumin ya ce: Eh, na yi tafiya. Ya ce masa: Kuma yaya ka yi tafiya a cikinta? Mutumin ya ce: Na ga ƙayar sai na nisance ta, ko na tsallake ta, ko na guje ta. Sai Abu Huraira Allah ya yarda da shi ya ce: Haka taƙawa take.