Ranar Albarka ta 'Arafah
Assalamu alaikum yan'uwa masu daraja. Ranar 9 ga watan Zulhijjah, ranar 'Arafah, hakika ranar ce mai matukar muhimmanci. Ita ce ranar da Allah yake 'yantar da rayuka daga wuta fiye da kowace rana-kamar yadda Manzo ﷺ ya fada a Sahih Muslim. Don haka mu yi iyakar kokarinmu don mu cika ta da ibada, tuba ta gaskiya, da addu'o'i na zuci. Azumin wannan rana yana da matukar alheri domin, kamar yadda Manzo ﷺ ya ce, yana share zunubban shekarar da ta gabata da wacce za ta biyo baya (Muslim). Kuma idan ana maganar addu'a, Manzo ﷺ ya ce mafificiyar addu'a ita ce wadda ake yi a ranar 'Arafah, kuma mafificin kalmomin da za a fada su ne: "La ilaha illallahu wahdahu la sharika lah, lahul mulku wa lahul hamdu wa huwa 'ala kulli shay'in qadir." Imam al-Baji ya bayyana cewa wannan addu'a tana dauke da albarkoki mafi yawa, lada mafi girma, kuma ana karva ta da sauri. Don haka kar a rasa wannan dama. Zubo zuciyarka a cikin addu'a don kanka, matarka, yaranka, da dukkan Al'umma. Ka tuna da Musulmin da ke shan wahala a Palasdinu, Sudan, Kashmir, da sauran wurare. Ka yi Salati ga Manzo ﷺ, kuma don Allah ka saka ni a cikin addu'o'in ka. Jazakum Allahu khayran. Wassalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuh.